Tuesday, March 20, 2012

Dama Ba Ta Karewa

DAMA BA TA KAREWA

Ba kamar yau na gamu da babendaliyar budurwata, Halima ba, amma kamar yau na kama makwanci a unguwar Kofar Nassarawa da ke cikin birnin Kano . Kamar yau sa’idawan unguwar suka shaida mini cewa ban isa ba, bayan tun isa na da dadi na gama sanin cewa na isa. Haka kuma, kamar yau sa-toka-sa-katsin da har sai da ya yi sanadiyyar yayata al’amarin a kafofin yada labarai, ya afku, wanda ta sanadiyyar hakan har hukuma ta shiga al’amarin ta hanyar aika mini da takardar kira, wanda ga ni yanzu na amsa kiran.
Ko kusa ban yi mamaki ba da na iske cikin wadanda za su jagoranci ganawar har da manyan mallamai guda biyu, baya ga wakilan hukuma. Bayan sharar fagen zaman, sai jagoran zaman ya ce mini, “Labarin da muke da shi shine, ka zo da bakon abu, inda duk wayewar garin duniya wata mace, wadda ba ka da shaidar kasancewarta muharraamarka, kan je makwancinka, bisa ga amincewarka, ta dafa maka abinci, kana ta tafi. Tare da cewar mutanen unguwar sun sha nuna maka cewa hakan ya saba da koyarwar al’ada da addininsu.” Kana ya tambaye ni, “An yi haka?”
Cikin girmamawa na amsa da “Kwarai, an yi haka Ranka-ya-dade.”
“Kuma tunanin halin da za ka kasance ciki, idan tuburewarka ta fusatar da mutan unguwar har suka dau doka a hannunsu, bai taba shiga kwakwalwarka ba?”
Cikin girmamawa na kara amsawa da “Wannan tunanin ya shiga kwakwalwata tun ma kafin na tubure din, Ranka-ya-dade.”
“To mai ya sa ba ka bi doka ba don ka zauna lafiya?”
Na kaskan da murya, “Tare da girmamawa ga dokacin mutanen gurin nan, abin da na yi ni ban ga wani aibu a tattare da shi ba, baicin ta fuskar al’ada, wadda ba kasafai na fiye martaba ta kan al’amarin da baro-baro addini bai hore ni da guje masa ba. Ta yiwu karancin ilimin addini na damu na, amma abin da na san addini ya haramta shine kadaicewa ko mummunar cudanya tsakanin namiji da macen da ba muharramarsa ba. Idan aka dubi al’amarina da Halima ba za a iya cewa wancan hani ya shafe shi ba, don kuwa, Halima kan je masaukina da misalin goma na safe, sa’ilin da ba na dakin, ta dafa mini abinci, kana ta bar dakin bayan ta gama. Ba na ko tantama sanin da mutanen unguwar suka yi, na lokacin zuwa da tafiyarta, shine dalilin da ya sanya ba su dau doka a hannunsu ba. Amma abin da mutan unguwar ba su sani ba shine Halima na girka mini abinci ne don ni ban iya ba, gashi kuma sayen abinci kan iya tarwatsa bukatata ta adana wani abu cikin abin da nake samu, wanda ba shi da yawa. Kuma ina yin adanin ne don samun yadda zan yi in zama cikin yanayin da zan iya tunkarar kowane kalubale na aurar Halima. Don haka, bisa la’akari da bukatar aurar junanmu da muke da ita, gami da takurarren yanayin da muka zamo ciki, ya sanya muke yin abin da al’umma ke yi masa kallon rashin dacewa, maimakon taimaka mana da addu’ar Allah Ya cika mana buri. Wannan shine dalilina, amma na yi alkawarin idan mallaman dake wurin nan suka ga rashin dacewar yin hakan, to daga yau zan daina.”
Daya daga cikin mallaman ya dubi jagoran zaman ya ce, “Ina ganin idan da yadda hukuma za ta yi ta taimaka wa wannan bawan Allah wajen cimma burinsa, to ya kyautu.”
Haka kuwa aka yi. Hukuma ta saya mini gida, ta bani jari, ta kuma jagoranci daurin aurena cikin abin da ya gaza wata guda. A ranar da na shiga cikin dakin matata dake cikin sabon gidana na iske Halima, bayan mun kintsa kanmu, sai ta ce mini, “Har yanzu fa mamakin yadda aka yi har ka samu wannan damar nake yi.”
Na ce “To ki daina. Don tare da cewa duniya na fama da mashasshara, amma damammakin dake cikinta ba sa karewa, matukar dai anyi katarin iya amfani da mashassharar wajen yin sara kan gaba.”
AN KARANTA AN TACE A RANAR LAHDI 05/07/2009 YAYIN TARON ANA

Friday, March 9, 2012

Hudubar Shaidan

Hamisu ya yi tsaki ‘Mts.’

Ya yi tsakin ne bayan da ya kwashe tsawon wani lokaci yana kokarin tayar da jannareton wanda mirsisi ya ki tashi. Wani abin da ya kara kwarara fetur ga wutar bacin ran na Hamisu shi ne da karbo jannareton daga gurin gyaran, da ya haura sati guda, ba a fi sa’o’i biyu ba. Ga kuma tarin aiyukan mutane da suka haura mako guda a gurinsa, aiyukan da ba sa yiwuwa sai da wutar lantarkin da rashinta ya sanya ko taba aiki daya cikin tarin aiyukan da ya karba bai yi ba, tare da cewa tuni kudaden aiyukan da ya karba sun zama radaddu.

Sabi’u, wanda ke kallon duk ficikon da Hamisu ke yi da kagaggiyar zuciyar rashin samun aikinsa akan kari, ya ce, “Allah wadaran nasara. Ya rasa abin da zai yi sai abin dake bakanta wa al’umma rai.”

Hamisu ya nuna igigyar jannareton , ya ce, “Ita ma wannan shegiyar gajeriyar igiyar da laifinta.” Kana ya dubi Sabi’u, “Ko za ka zama igiya ne , in kara ka da ita, in gani ko hakan zai sanya injin tashi?”

Sabi’u ya yi shiru bai ce uffan ba. Kuma rashin cewa uffan din har cikin zuciyarsa. Yaya za a yi Hamisu ya shigo da maganar wasa cikin abin da ka iya janyo masa maimaita shekarar karshe ta karatunsa na jami’a? Wannan ya sanya ya dauke kansa daga kallon Hamisun. Hakan ya hana Sabi’u lura da lokacin da Hamisun ya koma ya shige cikin shagonsa. Lokacin da Sabi’u ya lura da Hamisun shi ne sa’ilin da ya fito daga shagon, rike da wata igiyar, wadda a ido ta fi waccan alamun kwari. Yanayin yadda Hamisun ya taho ya tuno wa Sabi’u da wani kakkarfan jarumin Hindu, sa’ilin da yake shirin tunkarar mugu, ta yadda da Sabi’un ya zamo cikin nishadi da ya yi wa Hamisu irin taken da aka rinka yi wa wancan jarumi wato daran-daran-daran.

Lokacin da Hamisu ya isa ga injin sai ya nannada igiyar kan matayar da injin yana muzurai, kana ya takarkare ya ja igiyar da karfin da ya sanya igiyar tsinkewa. Hamisu bai yi aune ba sai ji ya yi ya yi baya ya kuma fada kan Sabi’u, kana gaba-dayansu suka doku da garu. Kan Sabi’u ya kume a jikin garu, ji kake kuum!

Haushi ya kara turnike Sabi’u, ya yi shiru ya kasa magana har sai da Hamisun ya samu ya matsa daga jikin Sabi’u. Hamisu ya dubi guntuwar igiyar dake hannunsa, ya ce, “Wai da nasara ya kera jannareto, uban waye ya hana shi yin remote control a matsayin abin tashinsa?”

“Ina jin ubanka ne.” Sabi’u ya amsa.

“Kuturu!” Hamisu ya fada a harzuke, “Ka zage ni?”

Sabi’u ya amsa yana ciccije baki, “An zage ka din. Aiki fa na kawo maka, ba kwangilar wulakanta ni ba.”

Hamisu ya ce, “Ka ga kuwa, da ba ka kasance a kofar shagona, kada na cukurkuda ka a zarge ni da ragwanci ba, da jikinka ya gaya maka.”

Sabi’u ya ce, “Kana ganin cinta kenan!”

“Da shanta, da hadiyarta kai har ma da kasayarta ina gani.” Inji Hamisu.

Sabi’u ya ce, “To idan ka cika shege ka biyo ni.” Kana ya juya ya nufi bakin titi a kufule, yayin da Hamisu ya bi bayansa, shi ma a kufule. Da yake tuni har karfe taran dare ta gota, sai da suka yi jira na kusan mintunan rubu’in sa’a kafin su samu babur. Dan acabar da suka samu shi ma matashi ne kamar su. Ya tambaye su, “Ina zuwa?”

Sabi’u ya amsa, “Duk inda ka san za mu iya raba raini da wannan tsamin.” Ya fada yana nuna Hamisu.

Dan acabar ya nazarce su kafin ya ce, “Casuwa za ku je yi kenan.”

Hamisu ya ce, “Ai ka san su kananan shegu sai ana raba raini da su.”

Dan acabar ya ce, “Da kyau. Dama ban samu damar kallon damben dazu ba. Don haka, kyauta ma zan kai ku. Ku dai ku hau.”

Suka kuma hau. Hawan da bayan tuki na tsawon lokaci suka isa wani guri wanda ya cika dukkanin sharuddan gurin da suke nema. Dan acabar ya yi fakin yayin da suka sauka. Hamisu da Sabi’u suka shata da’ira amma kafin su fara abin da ya kawo su sai dan acabar ya ce, “kafin fara kallon fadan, zan so sanin dalilin fadan idan da hali.”

Sabi’u ya nuna Hamisu, “Laifinsa ne…”

Dan acabar ya dakatar shi, “Dalilin kawai nake son sani.”

Suka buda masa hoto mai kala na al’amarin da ya janyo rikicin nasu. Dan acabar ya ce, “To ai wannan dalilin bai kai ku ji haushin juna kansa ba. In har za ku ji haushin wani to haushin wandanda alhakin bayar da wutar lantarki ya rataya a kansu ya kamata ku ji.”

Wannan lafazin ne madigin da ya diga ayar karshe dangane da batun raba-rainin da Hamisu da Sabi’u ke shirin yi. Hamisu ya dubi Sabi’u, “Haka ne fa Sabi’u, haushin kazar rashin cikar burinka bai kamata ya huce kan damin raunina ba.”

Hamisu ya ce, “Ko dai kana nufin ka ce naka raunin bai kyautu ya kullaci nawa ba.” Kana gabadayansu suka tintsire da dariyar da a karshenta Sabi’u ya ce, “Gaskiya duk ranar da duk na samu wata dama ta mulkar al’umma to ya zama wajibi in huce haushina. Don wallahi cinye-du zan zama.”

Sabi’u ya ce, “Kai dai bari in kammala digirin in samu wata dama. Sai na warci duk abin da zan iya na kowane irin kudi da zai gilma ta kasan tebirina. Ni kam wartau zan zama.”

Dan acabar, wanda ke sauraronsu, ya yi ajiyar zuciya, “Ai na yi tsammanin rashin adalcin da ya shafe ku zai karfafa maku gwiwa ne wajen ganin guje shi, sa’ilin duk da ku ka samu dama, la’alla ko na kasanku sa taso da kishin kasa na hakika.”

Hamisu ya ce, “To kana kuwa bukatar sake tsammani. Domin babu abin da zai sanya ni sauya wannan niyya tawa.”

Sabi’u ya ce, “To ai ni, tun da na kusa gama shan tawa wahalar, ba ma na so a samu sauyi wajen tafiyar da jagorancin al’umma. Kasa ma ta fi dadi ga bunkasasshe idan ba a martaba doka, kuma talauci da alfarma suka yi yawa.”

A nan sai dan acabar ya ce, “Ashe zuciyoyinku ne suka gurbata shi ya sa ku ka dace da shugabanni. Kuma na yi imanin haka zuciyoyin akasarinku suka gurbata. Ku kuma rike wannan cikin zuciyarku cewa sai kun yi nadama.”

Hamisu da Sabi’u suka bushe da dariyar da ba ta tsawaita ba. Wannan ya faru ne kuwa saboda bacewa da dan acabar gami da baburinsa suka yi. Ai nan take idanuwansu suka raina fata. Ashe baburin aljani suka hawo. Kuma kowannensu ya koma gida ne a tsure, kamar yadda kowanensu ya sanar da mutan gidansu abin da ya faru. Babban abin da ya fi damun kowannensu shi ne furucin dan acabar na karshe. Wannan ya haifar da gamuwar da mahaifansu suka yi, inda suka yi shawarwari, daga karshe suka samo mafita, wato kai kuka zuwa gurin mallam Batarsu.

Suka kuwa je gidan mallam Batarsu, wanda ke a wani kungurmin kauye. Sun iske wata kyakkyawar budurwa a farfajiyar maganar mallam, wadda da ita suka yi jira har mallam ya fito. Mallam Batarsu ya yi umarnin cewa gabadayansu su shiga, don haka da budurwar, da Hamisu da kuma Sabi’u suka fuskanci mallam, wanda ya fara magana, “Na yanke shawarar ganinku a lokaci guda ne saboda al’amuran da suka kawo ku suna da kamanceceniya.” Kana ya dubi budurwar da zai ce, “Ke kin zo ne saboda neman tallafin gano inda bataccen mahaifinki yake. Hakika mahaifinki na nan da ransa, kodayake dai yana cikin wani mawuyacin hali, kuma dab yake da rasa ransa. Kuma, yin sanadin kubutarsa daga wadanda suka kama shi kankanen abu ne a gare ni. Sai dai ba zan taimaka wajen fitowarsa ba ko nawa za a bani. Dalilina shi ne, gaskiyar mahaifinki ta yi yawan da nan gaba zai iya hure wa talakawa kunne su yi bore, ni kuma ba na son haka. Domin, idan yanayin bai zamo cukurkudadde ba to mutane irin mu ba za su samu kulawa daga gurin manya ba domin sana’armu ba za ta yi tasiri ba. Su kuwa, wadanda suka kama shi sun yi haka ne domin yin amfani da sassan jikinsa wajen yin wani asiri, wanda ba zai yiwu ba sai da sassan jikin mutumin kirki. Don haka nake ba ki shawara da ki dauka cewa rashin mahaifinki kamar wata hadaya ce da aka yi don kyautata rayuwar mutanen da suke da ra’ayin amfanuwa da sana’armu.”

Budurwar ta dube shi, “Ai ban san haka kake ba, da ban zo ba. Kamar yadda ka ce, za ka iya taimaka mini amma ba za ka yi ba, to ko da cewa ka yi za ka taimaka mini a kyauta ba zan karbi taimakonka ba. Na gwammace wa rasa komai da na karbi taimakon mugu.” Kana ta tashi a fusace ta fice.

Mallam Batarsu ya dubi su Hamisu ya ce, “Idan na so zan iya jifan ta da jafa’in da ka iya lahanta rayuwarta. Sai dai ba zan yi hakan ba kawai don ba ta yi wa mahaifinta irin gadon da albasa ta yi wa ruwa ba. Kuma kamar yadda nake son gurbatattu su yawaita a kasa, haka ma ba na fatan a nemi mutumin kirki a rasa a kasa, domin lokaci zuwa lokaci aiki kan taso mana wanda lallai sai da sassan jikin mutumin kirki yake yiwuwa.” Kana ya yi murmushi, “Ku kuma, tsoron da kuke ji na barazanar da karamin aljanin nan ya yi maku, ku daina shi. Irin ku na fi so ku yawaita a kasa. Yau din nan zan umarci Tuburzuku ya kamo mini karamin aljanin, da ya tsorata mini ku, ya daure mini shi a gidana. Daga yau ya daina yawo, ballantana har ya samu damar kara tsorata mini masoya irin ku.”

Sabi’u ya tambaya, “Ran mallam ya dade, wane ne kuma Tuburzuku?”

Mallam Batarsu ya bushe da dariya, “Ba ka san Tuburzuku ba, ko? Ai shi ne ke cin zalin aljanu ya kuma zauna daidai. Ka ga kuwa shi ya iya jan zare, ba jan-zare ba.”

Tarwatsewar Mafarki

Ba gargadi, ba zato ba kuma tsammani sai motar dake gabana ta tsaya cak a tsakiyar titin. Wannan ya sanya take birki cikin gaggawa da na yi ya yi rashin nasara ya kuma zama sular nasara. Rashin nasara wajen kasa hana gaban motata bugar bayan motar dake a gaban nawa, kamar yadda sular nasarar ta zamo bayar da dama ga gaban motar dake bayana ta bugi bayan motar tawa.

Batare da yunkurin gefencewa ba, sai, ganin direban motar gaban nawa ya fito, ni ma na fito yayin da direban motar bayana shi ma ya fito.

Da yake direban motar gaban nawa ne ya haifar da buge-bugen motocin, sai na yi zaton uzuri zai kawo, wanda da hakan ya yi da na ce masa kada ya damu mu fara gefencewa tukunna. Maimakon hakan sai kawai ya bangaje ni, ya fara aibanta tukina yana cewa shi ma’aikacin hukumar kare hadura ne, kuma shi bai taba fara barin filin daga ba don haka sai ya nuna mini kuskurena.

Ba kuma mamaki, tsoro ko takaici ne ya sanya ni yin shiru, na zuba wa sarautar Allah idanu ba, a’a, yakini da nake da shi ne na cewa, kamar dai yadda hargowa ke nuni da raunin guguwa, haka shi ma shiru ke nuni da karfin dutse. Kuma, ko su masu fara barin fagen dagar ai barin kamar zilliya ce wadda ta kasance salon yaki wanda shi kuma dan zamba ne kamar yadda Lincoln da Sun Tzu suka bayyana. Kamar yadda sayyidna Mu’awiyya ya bayyana. Haka kuma kamar yadda shi shugaban halittar kansa ya baiyana.

Direban da ya buga mini, tare da wasu da suka ga gaskiyar abin da ya faru suka rinka ba ni baki, suka kuma gargadi shi wanda ya fara bugawar da cewa, matukar ya cigaba da kokarinsa na aibanta ni to kuwa a shirye suke da zuwa ko ina ne wajen ganin sun shaide ni. Da dai ya ga babu sarki sai Allah sai ya yi kwafa ya tafi. Kana suka kara ba ni hakuri, inda na gode masu dangane da kasancewarsu mutanen kirki.

Bayan komai ya lafa na shiga motata na bar gurin, sai kirkin wadannan mutane ya rika bijiro mini. Na tuna da yadda suka kashe wutar da kuma yadda suka yi ta ba ni baki. Da sun san ni da sun san cewa kashe wutar kawai da suka yi ma ya wadatar, da ba su dage da ba ni hakuri kan na kyale mutum da aniyarsa don samun maslaha domin kuwa murhun garwashin wutata ya yi sanyi.

Murhun garwashin wutata ya yi sanyi!

A wani yammaci, lokacin kuruciyata, an yi iska mai matukar karfin da har ta rakakkabo jemagun dake kan wata bishiyar dabino dake a gewayen gidanmu. A wancan lokaci, farin cikin da mu ka yi, ni da abokina Sanusi, shigen irin wanda makalaci kan yi ne sa’ilin da ya tsinci dami a kalansa. Ba mu yi wata-wata ba muka tattara wadancan jemagu cikin wani buhu, kana muka tunkari gidan mista Tunde bisa ga tunaninmu na sayar masa da jemagun, tun da an taba shaida mana cewa bayerabe ya samu jemage kamar mu ne mu samu naman kaza.

A kan hanyarmu ta zuwa gidan mista Tunde muka rinka tattauna yadda kowannenmu zai yi da nasa kason kudin jemagun. Yayin da Sanusi ke da burin sayo kura don ya rinka sanya ta tana cinye duk wadanda ke cin zalinsa a makaranta, ni burina ga kudin bai huce sayo giwa ba. Giwa mana, wadda zan boye ta har sai ranar hawan Nassarawa in hawo abata. Sauran mutane a kasa, wasu a kan dawakai, ni kuma akan giwa! Dole a kalle ni.

Amma al’amarin bai tafi yadda muka zata ba. Da muka kai wa mista Tunde jemagun muka kuma shaida masa dalilin kai masa jemagun, maimakon hakan ya burge shi, ina! Sai ya tunzura ya biyo mu da duka yana korafin wai mun raina masa wayo. Da kyar dai kafarmu ta kwace mu a waccan rana.

Har kullum na kan lura da wancan al’amari a matsayin notin da rayuwata ta rinka juyawa kansa. Tunanin hawa giwa lokacin hawan sallah tunani ne dake nuna tsantsar tasirantuwa da karfin iko gami da tsananin bukatar fin karfin kowa da komai. Kodayake dai, shan bamban da al’amarin ya yi da tsammaninmu a wancan lokaci ya sanya na ji a jikina cewa na rasa wani abu amma ko kusa rashin bai dakushe mini karfin gwiwa ba. Na cigaba da kai-kawo wajen ganin na cimma babban matsayin da babu kamarsa. Ta haka na zurfafa a karatun bokon da har na zama furofesa. A wancan yunkuri, na je manyan birane na manyan kasashen duniya da dama.

A wasu kasashen na ga kishin kasa na gaske, wanda mu ka rasa ga shugabannin kasar nan, amma ban ga kwanciyar hankalin shugabanni ba. Na ga kimanta alkawari da bin doka amma ban gano watayawa ba. Na gano tausaya wa ‘yan kasa maras sa karfi amma ban gano alfarma ga malalaci ba. Na ga tasirin sahihanci amma ban gano ingancin rudu ba. Na jiyo kamshin abinci amma ban ji daidaitaccen dandanonsa ba. Tirkashi! Kusan a duk inda na gano wani abu mai matukar muhimmanci da muka rasa a kasarmu, na kan hango wani amfanu da rashin nasa ke da shi ga wasu a kasar tamu, wanda tabbas za a iya samun masu bukatar irin wannan tsarin a kasashensu. Ga shi ni ma duk da matsayin farfesa da na kai amma matsayi guda kawai hakan ke iya wakilta.

Shin, me ya sa mutum ba ya taba iya zama ba tare da wata damuwa ko wata bukata cikin zuciyarsa ba? Me ya sa mutum ke iya jinginar gona amma sai ya kasa noma ta? Ko wanda ya iya nomawa ya kasa girbewa, wanda ya girbe ya cashe ya kasa surfawa, ko a iya surfawa, a kuma iya dafawa amma a kasa taunawa? Me ya sa mutum ba ya taba zama kwararren da zai iya gamsar da kansa a komai ba?

Amsar ita ce mutum ba shi ya yi kansa ba, ba kuma shi ke tasarrafi da rayuwarsa ba. Wanda Ya yi shi Shi ya san yadda ya tsara al’amuransa don alaka tsakaninsa da ‘yan uwansa ta kyautata. Shi ne Allah Mai kaga mutum Ya kuma sarrafa tasirin al’amuransa. Tsarki ya tabbata gare Shi. Aminci kuma ga manzonSa.

Kuma na fahimci hakan, fahimta ta goguwa dake samar da ilimi ba ta karatu wanda ke samar da shaidar an yi ba.

Sai Da Ruwan Ciki

Ban kasance cikin jerin mutanen nan dake da halayyar kin tashi, har sai an tayar da su, sa’ilin duk da bangazau ya bangaje su ba. Na fi yarda da in kokarta mikewa da kaina don cigaba da halattacciyar rayuwata. Dalilin kenan da ya sanya na bijire wa dabi’ar nan ta sa’idanci, ta’addanci da bambadanci lokacin da na tsinci kaina cikin dimbin sallamammun ma’aikatan gwamnati a wani abu da ya fi kama da takidin kara talauta talautattu da kara bunkasa bunkasassu.

Bukatar cigaba da tsayawa kan siraran kafafuwana ta hadu da karancin hanyoyin samun kudi wajen haifar da hadowar hadirin talauci wanda ya tayar da guguwar gazawar da ta hargitsa kurar kuncin maraici gami da kadaicin da bai bar ni da wani zabi bayan yanke shawarar barin garin ba.

A ranar da na daure jakata na hau mota, abin da na sani shi ne birnin Kano na nufa amma abin da ban sani ba shi ne tafiyar wata aba ce da da na kasance boka to watakila da almutsutsaina sun tsegunta mini abin da zai biyo baya.

Kurnar Asabe ita ce unguwar da na sauka a birnin na Kano. Kasancewata bakon da ya je neman kudi gurin da bai san kowa kuma kowa bai san shi ba ya sanya ni fahihmta, a kasa da wata guda, cewa rashin samun aikin karfin da nake yi ya faru ne saboda dalilai biyu, wato rashin afkin jikina da kuma sifata ta ma’abota barci.

Da yake ban yarda akwai matsalar da ba ta da mawarwari ba sai na dau mataki kan waccan matsala. Matakin da na dauka ya zamo bin manyan kwatocin unguwar ina yashewa batare da kowa ya sanya ni ba. Manufata ta yin hakan ita ce la’alla ko hakan ya kawar da kallon rago da ake yi mini. Amma ina! Abin bai tafi yadda na so ba, don kuwa maimakon hakan ya kawar da wancan kallon da ake yi mini sai ya taimaka cikin dan kankanen lokaci abin ya tambara a unguwar cewa sabon mahaukaci ya bayyana.

Kallon mahukaci da aka rinka yi mini abu ne mai dakushe karfin gwiwa amma bai dakushe karfin gwiwata ba. Hasali ma wakar tsokana da yara suka rinka yi mini idan su ka hange ni ba ta taba sa wa na tanka masu ba. Tabbatar maganar nan ta masu hikima da suka ce Jigatar ruhi ne sirrin samun sahihiyar hikima sai hikimar waka ta rinka zuwar mini sa’ilin duk da nake cikin kwatamin. Ranar da ta zamo tauraruwar da ta haska wadancan kwanaki ita ce ranar wata asabar da safe. Ina dab da shiga wata kwata sai maigadin wani kayataccen gida ya zo ya ankarar da ni dangane da bukatar ganina da maigidansa ke yi. Don haka sai na bi bayansa har zuwa cikin gidan.

Mun iske maigidan a farfajiyar gidan tare da wata kyakkyawar budurwa, kowannensu na zaune kan farar kujerar roba. Bayan mun gaisa, sai mai gidan ya ce mini, “Sunana Dakta Abdu Nakowa. Wannan kuma,” Ya fada yana nuna budurwar, “’yata ce, Maryam. Kasancewarta dalibar jami’ar da aka uamrta da yin bincike kan wata cuta, wadda yanayinka ya sanya ta yi zaton cutar ta shafe ka, ya sanya ta son jin ra’ayoyinka kan wasu batutuwa. Idan ka yi mata kyautar lokacinka to za ka same ni cikakken mutumin dake yaba kyauta da tikwici.”

Da na waiwaye ta don jin abin da take son jin ra’ayin nawa kansa, sai ta fara da, “Abubuwan da kake yi sun sanya ka yin tambari a unguwar nan. Yayin da a bangare daya ka kan kaskantar da kanka wajen yin aikin da bai damu da lada ba, a daya bangaren kuwa halayyarka ga yaran dake tsokanarka ya sha bam-ban da yadda ya kyautu ka yi in har tsammanin da ake yi maka, na mahaukaci, gaskiya ne. Wannan ya sa ka yi mini kama da wanda ke da ruhin masu hankali da na masu rashin hankali duka a jiki daya.” Ta kura mini ido da za ta ce, “Ya kyautu kuwa in gamsu da hanyar da na bi wajen tunkararka a matsayin mafi sauki?”

“Na dauka ma ba za ki kare tambayarki da alamar tambaya ba,” Na fada ina mai nazarin dara-daran idanuwanta, “amma tun da an yi haka, amsata ita ce eh a’ah.”

Ta bida, “Me kake nufi?”

Na amsa, “Hanyar da ki ka bi tana da sauki amma ba ita ce mafi sauki ba. Hanya mafi sauki ita ce ta hanyar mamayar ruhin nan da bature ya kira hypnotism. Da kin yi amfani da wannan hanyar, da ki na dakinki ni kuma ina kwata, ruhinki zai mamayi nawa ki san duk abin da kike bukata daga gare ni ba tare da kin tsaya, gaba da gaba da ni ba. Hakan zai saukaka miki wajen yanke shawarar a ajin masu fama da tagwainiya (schizophrenia) da ya kamata ki sanya ni, a ajin paranoid ko na psychic?”

Wannan dan jawabin ne ya zamo mashimfidin da ya shimfida shimfidar gamsuwa da Maryam gami da mahaifinta suka yi cewa ban zamo cikin masu fama da cutar schizophrenia ba face takurarren mutumin da tsattsauran tarnakin da rashin sa’a ya yi mini ya sanya mutanen unguwar suka kasa fahimtata. Kuma ta dalilin haka Dakta Abdu ya yi mini alherin da ya ba ni damar zabar daya, cikin wakokin da na kirkira, wajen tace ta na kuma buga ta.

Wakar, mai baituka talatin, ta yi matukar karbuwa lokacin da na sake ta. Biyo bayan wakar farkon na fito da wasu mafiya ma’ana da dadin sauraro wadanda tabo mabambantan bangarorin rayuwa da suka yi ya sanya sunana ya karade kasar hausa cikin lokaci kankane.

Ban yi aune ba sai tsintar kaina na yi kan dokin farin jinin da ya rinka sukuwa da ni a fagen nasarar da, kasancewata cikinsa na tsawon shekaru ya ba ni damar kammala abubuwan da a baya na samu tawayarsu. Na yi auren da aka samu rabon jariri.

Ta dalilin tasirin da wakokina ke da su a harkokin al’umma ya sanya wata rana wani babban mutum ya bukaci ganawa da ni. Amma me? Manufar ganawar ita ce yi mini albishirin samun tsomuwa cikin kungiyar manyan kasa. A nan ya nuna mini wata takarda wadda ke dauke da sunayen mutane biyar, ciki har da sunana, wadanda suka yi sa’a aka shigar da su cikin wannan kungiya. Don haka rawar da zan rika takawa ita ce za a rinka ba ni abubuwan da ake so in rinka yin waka kansu domin cin nasarar kara ingiza al’umma zuwa inda ake so su ingizu. Inda ya kyasa mini cewa, baya ga tarin alfarmomi da za a rinka yi mana haka kuma za mu amfana daga janye tallafin shigowa da kayayyakin kasashen waje da gwamnati ke shirin yi.

Na taba yin mafrki an daga takobi za a sare mini kai. Da takobin ta taho gadan-gadan sai gabana ya yanke ya yi mummunar faduwa. Irin wannan faduwar gaban na ji lokacin da wancan babba ya gama jawabinsa.

Na dube shi, “Janye tallafin gwamnati daga kan abubuwan da ake shigowa da su kasar nan daga waje na fa nufin tashi da farashin komai zai yi a kasar nan. Hakan ai kamar kara jefa talaka cikin matsatsin rayuwa ne……”

Ya katse ni, “Matukar asirinka zai rufu me ruwanka da abin da zai shafi wani talaka. Kawai ka manta da wannan tsohon-yayin tunanin. Domin a yau muna cikin duniyar da gafiya ya kamata ta yi yadda duk za ta iya wajen tsira da na bakinta.”

Wannan batu nasa ya jefa ni cikin tunani. Wato duk da halin matsatsin da mafiya yawancin mutanen kasar nan ke ciki, wanda ya samu ta dalilin wawashe kudaden kasar nan da wasu tsirari ke yi, bai isa ba, shi ne aka bullo da wata hanyar ta kara takure su. Na zamo cikin tsirarin da za su amfana don kawai na cigaba da zama karen farautar masu son dawwama wajen dafe madafan iko!

Kodayake dai lokaci kan iya sauya komai amma na sha yin addu’a da kada Allah Ya kawo ranar da gatarina zai rasa abin sara baicin shuka. Domin, idan ban bai wa makaho sadaka ba bai kuwa kyautu in kwace sandansa ba. Wannan ce hujjata ta juya wa wancan kudiri baya. Juya bayan da, gudun kada in toni asiri, ya sanya suka tanada suka kuma sarrafa hujjojin karya wajen bayyana ni a matsayin cikakken mai aikata laifin karkashin kasar da kisa ne kadai hukuncina. Aka kuma tura ‘yan banga suka je gidana suka kone shi a matsayin hukuncin da mutane suka daukarwa kansu. Ta haka ran matata ya salwanta. Dan ne aka ci sa’a Allah Ya kubutar.

A lokacin da nake ta faman shan izaya a gidan kaso ne sai wata masoyiyar wakokina wadda ke da alakar nema tsakaninta da wancan babba. Ta yi shigar burtu, ta samo hujjojin da su ka karyata wadancan laifuka da ake tuhumata da shi, ta kuma gabatar da hujjojin a kotu. Kadayake dai daga baya ta rasa ranta, amma wata kakkarfar kungiyar duniya ta shigo lamarin, inda aka sake ni, aka kuma biya ni diyyar kazafi da kuma barnar da aka yi mini.

Tabbatar cewa gurbacewar duniya ya fi yadda na dauke shi tabarbarewa sai waccan kakkarfar kungiyar ta neme ni da su rinka amfani da ni ina munafurtar addinina. Fancakali da bukatar tasu da na yi ta sanya su ka kudiri aniyar dakusar da duk wani yunnkurin kara karfafa da zan yi. Wannan ya sanya na dauki dana na bar birnin Kano na koma gidan gonata dake kauyenmu.

Yanzu ne, da na kwantar da hankalina na samu damar fuskantar rayuwa. Ashe tarin kudi daban jin dadin rayuwa ma dabam. Ba kuma komai ke kara sanya jin dadin rayuwa ba illa kwanciyar hankalin da gamsuwar zuci ke bayar da shi.

Talakan da ya tsaftace zuciya da muhallinsa, ya kangare wa mutuwar zuciya da lalaci ya kuma fuskanci kansa, zai iya jin dadin rayuwa fiye da attajiri, mai mulki ko mallamin dake son ya fi kowa. Mutum bai isa ya fi kowa ba sai dai kawai ya taka rawar kidan da kaddararsa ta yi masa.

Hakika rashin kwantar da hankali ne sanadarin bata a rayuwa, kuma bayyanannen sakamakon ya kan zama ciwon zuciya ko kuma ciwon hauka. Kwantar da hankali kuwa shi ne ruwan cikin da sai da shi a kan janyo na rijiyar nasarar rayuwa.

Kuma, ga wannan gabar, ambaliyar kogin nazarin wani sashe na rayuwa ya kawo ni.

Tusa Ba Ta Hura Wuta

Ni dai mutum ne, kuma al’adar mutum ce ya yabi kansa kan wadansu abubuwa da yake tunanin ya kyautu a yaba masa, ya kuma gaza samun hakan. Don kuwa, baya ga idanuwana dake da saurin gane mutumin da na taba gani, ko da kuwa gani ne na dan kankanen lokaci, haka kuma kunnuwana ke da saurin shaida muryar mutumin duk da na taba hulda da shi.
Al’amarin da kan iya tabbatar wa da kowa cewa yabon kan nawa ya cancanta ya faru ne a hantsin wata lahadi, sa’ilin da nake hutawa da dunkufaffen kai, kan wani dakali wanda ke nesa da unguwarmu. Murya na ji ana yi mini sallama, kuma tun daga jin muryar kyakkyawar kwakwalwata ta shaida mini mai ita. Don haka da na dubi mai sallamar ban yi mamaki ba da idanuwana suka tabbatar mini cewa shi ne, wato talikin da ya taba shaida mini cewa sunansa Alaramman Fata. Mutumin da na yi la’akari da kallon fuskarsa wajen yin imanin cewa bai gane ni ba.
Kimanin shekaru shidda baya na taba tsintar kaina a kafe cikin lakar son samun kudi ba tare da wahala ba, duk kuwa da cewa sai na yi wahalar ya kamata a ce na samu. A wancan lokacin ne, yayin da nake dawowa daga Jami’ar Maiduguri, na hadu da wannan mutum, inda ya baiyana mini takensa ya kuma kalallame ni ya raba ni da kudaden hannuna, a madadin wata laya wadda ya gwada mini yadda ake yin kudi da ita. Ba mu jima da rabuwa ba kuwa na gane cewa damfara ta ya yi.
Na amsa masa sallamar, kana na fahimci batunsa. Ashe wai wannan ne zuwansa Kano karo na farko, kuma bai da wanda zai je gurinsa, ga kuma tsantsar yunwa da yake ji, dadin dadawa kuma bai da ko kwabo. Don haka ya kwantar da murya yake neman in taimake shi da abinci da kuma masauki.
Na ce, “Tabbata kai ni aka yi idan ka gan ni a Lahira.”
Ya ce, “Me ka ce?”
Na ce, “Cewa na yi wannan abar da ke hannunka ba waya ce mai tsada ba?”
Da ya amsa da ‘Eh’ sai na ce masa ni ma neman inda zan fadi in mutu nake yi. Don haka taimako daya da zan iya yi masa shi ne, zan raka shi inda zai fansar da wayar, da inda zai sayi abinci mai kyau. Maganar masauki kuwa ma yi ta bayan ya natsu. Da yake bai da wani zabi bayan hakan sai ya amince.

Mu ka je ya fansar da wayar kan kudi naira dubu goma, kana na raka shi kofar maciyar abinci ta Sterling Restaurant. A kofar maciyar na ce masa, “Nan ne inda za ka ci abinci a duk garin nan ka san ka ci, kai hasali ma turawan Ingila ne suka kafa gurin, kuma da sunan adadin kudinsu ake biyan kudin abincin.” Da ya tambaye ni dangane da tsada kuwa, sai na ce masa, “Ya danganta da yadda kake kallon tsadar. Bambancin shi ne ko ka san Abin da bahaushe ke cewa ‘fan daya’ Inda ya ce, ya sani.

Na kuma san zai ce ya sani din, don kuwa bahaushe kan kira naira biyu a matsayin fan daya.
Don haka sai na ce masa, “To abincin fam hamsin ma sai ka bar shi.”
Ya ce, “Ka ce ma duk abin rudu ne. Yo ko abincin hausawan zan ci ai na ci na naira dari.”
A wannan zaton nasa mu ka shiga, ya sa na sa aka kawo masa abincin fan hamsin. Bayan an kawo masa ya fara ci, sai na ce masa “Ka san abincin nawa kake ci kuwa?” Ya ce “Ba ka ce na naira dari ba ne?”

Na girgiza kai “Ni ban ce maka haka ba. Abin da na ce maka shi ne abincin fam hamsin kake ci, kuma duk fam daya na Ingila dai-dai yake da naira dari biyu da hamsin. Don haka abincin hamsin sau dari biyu da hamsin kake ci. Idan ka lissafa za ka ga abincin naira dubu goma sha biyu da dari biyar kake ci. Kuma kana da dubu gomar da ka jinginar da wayarka ka same ta, don haka idan ka gama za ka ba su dubu gomar, ya rage nasu su sa jami’an tsaron gidan su cukurkuda ka. Ka ga bayan ka fita sai ka cigaba da damfarar al'umma ta hanyar sayar masu da layar yin kudi.”
Kallon farko da ya yi mini ya tuno mini da kwantaccen dannannen ragon da ya hango mallamin yanka. Amma daga baya sai wancan kallon ya gushe, yayin da fuskarsa ta washe. Ya ce, “To fa! Wannan ramuwar gayya ce kenan. Sai dai na san a gare ni dama ba ta karewa. Kai ma kuma yana da kyau ka sani cewa ba kasafai tusa ke hura wuta ba.” Abu na gaba da na ga ya yi shi ne mikewa tsaye inda ya je gurin wani ma'aikacin gidan, bayan sun dan yi magana, sai ya koma tsakiyar dakin cin abincin ya yi gyaran murya ya ce, "To Jama'a, na shigo nan don cin abinci cikin rashin sani. Na dauka abincin fan hamsin na nufin biyan naira dari, sai bayan da aka zubo abincin na kuma fara ci sannan na gane fan hamsin din na nufin dubu goma sha biyu da dari biyar, kudin da ban taba mallakar adadinsu ba a rayuwata. Don haka nake son jama’a a taimaka a zo a taya ni ci in ya so sai mu yi karo-karo mu biya kudin. Amma ko ina da kudin, ni kadai ba zan iya cin abincin dubunnan nairori a lokaci guda ba.”

Hausawan gurin kuwa suka ce me za su yi in ba dariya ba? Hatta fararen fatun dake cin abinci a gun sai da suka rinka tambaya, da aka fassara masu abin da ya ce sai su ma suka rinka dariya. Ai nan take wani saurayi, wanda budurwar da yake tare da ita ke ta dariya, ya taso ya biya wa Alaramman fata kudin abincin. Kamar almara, a nan sai na ga mutane su na ta yi masa kyautar kudi. A nan na fice daga dakin cin abincin , na kuma bar gidan abincin.

Ko don rashin samun cikar buri ne ya sanya kwakwalwata dulmiya cikin tunani? Wato da ace burina na daukar fansa ya cika da tuni Alaramman fata na nan cikin wani mawuyacin hali. Abin tambayar shi ne me kasancewarsa cikin mawuyacin hali zai kare ni da shi? Ban dauki wani tsawon lokaci ba na gane cewa babu abin da zan karu da shi baicin gamsuwa. Irin gamsuwar dake hana sabuwar gwamnati dorawa kan aikin da tsohuwa ta fara matukar an samu sabani da jagororinta. Irin gamsuwar dake hana yin adalci tsakanin mutane biyu da suka samu sabani, wanda hakan yana matukar hana kasa cigaban da ya kamace ta. Mafita a nan ita ce a rinka rama naushi da rangwame maimakon a rinka rama shi da naushi.

Na dubi bakar kwaltar da motoci ke ta dawafi a kanta, kana na tuno da abin da Alaramman Fata ya taba fada, Tusa Ba Ta Hura Wuta! Kuma haka ne, domin da na kasance fasihi da na raka amshin wannan waka da daidaitattun baitoci,

Shi Jini Launinsa Ja,

Lauya Takamarsa Hujja,

Wanga tsari ya sa tusa

Ko Wuta Ba ta Hurawa

Bakin Dare

Sai bayan gotawar karfe daya da rabi na dare batare da alamun karfin jikin da nake ji ya soma raguwa ba, illa iyaka ma karuwa da yake, sannan na ankara cewa ta yiwu babu ni a cikin wadanda ke da rabon yin barci a daren.

Gashi dai kwakwalwata na matukar bukatar hutu amma idanuwana tangararau. Jikina kuwa ji nake kamar yana tsikari na saboda tsantsar kwarin jikin da nake ji yana kara mamaya ta. Na yi kwafa na cillar da littafin da na jima ina dubawa, kana na mike zaune. Shin mene ne dalilin da ya sanya daren na yau ya bambanta da sauran a gare ni?

Bayan ninkayar da na yi ta yi cikin kogin tunani sai na gano cewa hakan ba zai rasa nasaba da shayin da na sha a farkon daren na yau ba. Shayin da dandanonsa gami da gurin sayar da shi ya sha bamban da na saura.

A lokacin da karfe biyun dare ta gota sai na ji ba zan iya cigaba da zama cikin daki ba, don haka na mike, na bude kofar shagona kana na fito waje. Na kalli dogon layin, wanda farin wata ya matukar rayawa da dan karen hasken da duk da matsalar rashin wutar lantarki amma ban samu matsala wajen gano aibun layin ba. Babu shakka, babban aibun faffadan kwararon shi ne rashin lambatu. Don haka mai zai hana na yi kishin kasa na haka lambatun cikin daren ta yadda sai dai mutanen unguwa kawai su wayi gari da aikin da na yi? Ta yiwu ma jin dadin aikin lambatun ya sanya a ba ni mai-unguwar unguwar duk kuwa da kasancewata ba zuwe a unguwar.

Sai dai me? Haka ba ya taba yiwuwa da yatsun hannu wadanda su kadai ke gare ni a ababan da za a iya aiki da su. Wannan ya sanya ni tunanin inda zan samu magirbi da diga da shebur wadanda da su ne kadai aiki irin wannan yake yiwuwa. Shin ina zan same su?

Kamar amsa ga wannan tambaya tawa sai cikina ya kada, alamar dake ishara da bukatar yin juyen bahaya nan ba da jimawa ba. Don haka na kama hanya na nufi dakina wanda cikinsa ne bandakina yake. Sai da na je dab da shiga sai na ja na tsaya. Me zai hana na tunkari bola don yin juyen bahayan? Domin idan na ci sa’a ma na iya yin tsintuwar kayayyakin aikin da la’alla wani birkila ya manta. In na yi wannan sa’ar kuwa to na kashe tsintsaye biyu kenan da dutse guda.

Wannan ya sanya na juya na nufi hanyar da za ta kai ni bolar dake bayan gidan Alhaji Bello Matsolo. Haka na yi ta tafiya har na isa karshen kwararon, kana na mike kwaroron da bolar da na nufa take. A lokacin da na isa kofar gidan Alhaji Bello Matsolo tuni har bahayan da nake ji ya matso ni, don haka da sassarfa na karasa bolar na kuma shiga ciki ina tunanin inda ya fi kamata na juye bahayan. Kallo daya na yi wa bolar na hango wani abu tullulu mai kama da kifaffen tulu, don haka sai na karasa gurin na sa kafa da zummar buda shi.

Abubuwa biyu ne suka sa bahayan da nake matukar ji ya bace bat. Na farko dai, da kafata ta shuri abin sai na ji shi lagwaigwai, alamar da ta tabbatar mini cewa abu mai rai na shura. Na biyu kuwa shi ne gwauron numfashi da abin ya yi, kana a hankali sai na ga wani abu a gefena ya motsa. Da na lura sosai sai na ga abin ashe hannu ne ya yaye wasu tsummokara dake kusa da ni sa’ilin da kan abin ya bayyana, kana ya mike tsaye cikin zafin nama ya dube ni.

Da ban kasance cikin tsantsar rudani ba da hakika na tintsire da dariya. Abin, mai sifar mutane, bai yi mini kama da komai ba in ban da shirgicecen mutum mai tullukeken ciki kamar randa. Dadin-dadawa kuma, ba ya sanye da komai a jikinsa in ban da wani bujukuran gajeren wando. Amma ina! Haka nan na daskare a tsaye ina jiran ya yiwo kaina ya halaka ni.

Maimakon hakan sai na ga ya juya da gudu ya bi ta cikin bolar har ya je karshenta, inda daga nan sai ya bulle ta daya kwararon ya yi tafiyarsa. Bayan shudewar wasu ‘yan dakiku sai na dawo hayyacina. A rude na fito daga bolar bisa ga burina na komawa shagona. Amma da yake a rude nake, sai na kara nitsa cikin kwararon maimakon in fita daga shi.

Can sai na hango hasken fitilar da na yi zaton na mota ne, don haka sai na rage gudu ga zatona na cewa wani Alhajin ne ya yi dare. Ta yiwu idan na yi masa bayani ya taimaka ya rage mini hanya zuwa dakina. Da motar ta karaso, na tsayarta sai ta tsaya. Don haka sai na karasa kofar direba. Ina dab da fara yi masa jawabi sai ji na yi an damke ni ta baya. Na yi kokarin kwacewa amma ina! Wanda ya damke nin ya fi ni karfi, nesa ba kusa ba. Kana sai na ji wata kakkaurar murya na yin magana a barin kunnena na dama.

“Kada ka bata lokacinka, samari,” muryar ta cigaba da fadin, “Don kuwa ba za ka iya kwacewa ba. Ta yiwu idan kana da dogon kwana ka kwace a can gurin yanka, amma ba daga hannuna ba.”

Hakan da kuma kamshin turaren dake tashi daga jikinsu ya tabbatar mini cewa ‘yan mafiya ne. A karo na biyu, tun bayan fitowata daga dakina, sai kwakwalwata ta kara tsayawa. Ba ta tashi cigaba da aiki ba sai da na ji direban motar na cewa wanda ya rike ni, “Sake shi Baba, ba mutum ba ne. Dubi karshen inda hasken fitilar motar nan ke haskawa. Ga dan’uwansa can yana tahowa.”

Ban tashi gane abin dake faruwa ba sai bayan da na ji an sake ni, na kuma kalli gaban motar na hango halittar nan da na taso a bola. Sai yanzu, da fitilar mota ta haske shi sannan na ga ashe kurtsetsen cikin nasa launin toka ne kamar yadda fuskarsa ma ta zamo hakan. Da da rana kuma cikin jama’a aka gan shi sai a yi zaton tashe zai je.

Tun kafin motar ta gama yin ribas na fita da gudu. Na bi ta wani lungu kana na sha kwana. Shan kwanar tawa da wuya kuwa sai na ji na taka wani abu mai laushi, wanda daga baya na gane ashe cikin masifaffen kare na taka. Na gane haka ne ta hanyar jin haushin da karen ya rinka yi sa’ilin da ya biyo ni ya kuma rinka hankoron cafar agarata. Wannan ya sa na kara gudu kamar raina zai fita. Har na isa layin Bello Matsolo karen bai daina bi na ba ni ma kuma ban daina gudun ba. Hasali ma ta kasan wata bishiya na huce, bishiyar da ake tsoron tunkararta saboda tarin kudan zuman dake kanta. Ina karya kwana kuwa sai karen ya dako wani uban tsalle ya dira a gadon bayana, hakan ya sanya na fadi na yi rub-da-ciki. Cikin zafin nama, karen ya mirgine ya kara yi wo tsallen da babu tantama sai ya turmushe ni. A sannan ne na ji wata kara a lokaci guda kuma na ga wani haske mai kama da walkiya. Maimakon karen ya turmushe ni, sai ya fadi gefe guda ya mimmike.

Ban yi azarbabin yin ajiyar zuciyar kubuta ba har sai da na fara kallon inda hasken ya fito. Gabana ya yanke ya yi mummunar faduwa da na hango mutanen da yawansu ya kai biyar, kowannensu rike da bindiga. Ba na bukatar wasa kwakwalwata kafin na gane mutanen a matsayin ‘yan fashi da makami.

Ban san lokacin da na yi kukan kura na mike tsaye, kana na juya da baya na bi hanyar da na biyo ba. Ina karya kwanar kuwa sai na ji karar tagwan harsasai da suka harbo. Da dai ban ji wani abu ya shiga jikina ba sai kawai na cigaba da gudun da nake, yayin da na ji takun sawayen wasu cikinsu sun dafo mini baya. Wannan ya sanya na kara dagewa bisa ga aniyata ta kai wa mararraba don kara karya wata kwanar. Amma abin bai tafi yadda na so ba, domin kuwa ina karya kwanar sai na yi karo da wani kakkarfan abu, wanda, saboda tsantsar gudun da nake yi sai da muka fadi tare da shi. Na hanzarta mirginewa na dube shi na kuma gane shi a matsayin mai kurtsetsen cikin abin nan da na taso shi a bola. Bambancin kawai shi ne wannan karon sai ya yiwo kaina ya turmushe ni, da na yi yunkurin yin kara sai ya sa wani abu mai kama da hannu ya rufe mini baki. Kana ya yi mini magana cikin rada, “Kada ka mike tsaye. Barayin da suka biyo ka gidana suka je. Ni ne Alhaji Bello. Kada ka yi motsi. Kwanta kawai abinka. An ce idan mutum na da hakuri akasarin matsalolinsa kan warware kansu da kansu.”

Na kuma kwanta na kuma yi shiru amma ba don na gamsu da shawararsa ba, sai don ba yadda zan yi. Ai kuwa sai na ji karaji da hayaniya gami da tarwatsewar mutanen da na tabbatar su suka biyo ni. Bayan dauwama da karajin ya yi na tsawon wasu dakiku sai mu ka ji shiru.

Sai daga baya na gane abin da ya faru. Ashe harsasan nan da ‘yan fashin suka harbo mini ne suka zarce kan bishiyar nan da kudajen zuma ke kanta, suka kuma tarwatsa kudajen zuman suka yo kasa, wanda cikin rashin sanin abin da suka yi, ‘yan fashin suka karaso da niyyar hucewa inda haushin kazar kudajen zuman ya huce kan ‘yan fashin.

Haka kuma ashe wannan kurtsetsen mutumin ya yi gaskiya da ya gabatar mini da sunansa a matsayin Alhaji Bello, wato Bello matsolo. Ashe ‘yan fashin gidansa suka je, inda ya ci sa’a ya hange su tun kafin ma su shiga gidansa. Kasancewar dokacin iyalansa sun yi tafiya, sai ya baro gidan, ya kuma yi bad-da-bami ta hanyar bursune jikinsa da toka ya kuma saje da tarkacen bola, inda a can na fara ganinsa cikin wannan dare.

Dadin dadawa, ashe ya ji karar harbin da ‘yan fashin suka yo mini, ya kuma yi zaton inda harbin zai je da abin da zai haifar. Wannan ya sanya shi ya rike ni gudun kada fantsamar kudajen zuman ta shafe ni

Duk na san haka ne daga baya, lokacin da bayan gushewar karajin ‘yan fashin, Alhaji Bello ya tashe ni, muka hanga kwararon inda muka hango gabadayan ‘yan fashin a kwankwance a kasan bishiyar.

Sai yanzu da na tabbata na yi cikakkiyar kubuta sannan na gane cewa hakika Alhaji Bello Matsolo ya yi dai-dai da ya ce, matsalolin mutum na iya warware kansu matukar mutum ya yi hakuri a rayuwa. Abin da kawai Alhaji Bello bai ce ba shi ne matukar mutum na da gaskiya. Tabbas tsanani ba ya dorewa matukar dai mutum bai bari tsananin ya karyar masa da zuciya har ya yanke kauna daga rahamar Ubangiji mai kowa mai komi ba. Ga mamakina sai na samu cewa na matukar amfanuwa daga bala’in da na shiga cikin wannan dare. Shin dama haka ne da masu hikima suka ce shiga taskun rayuwa na taimaka wa mutum wajen samun sahihiyar hikima? Idan ko haka ne, shin na yi adalci kuwa idan na kira wannan dare da bakin dare?

Ungulu Da Kan Zabuwa


Zai iya yiwuwa na yi rashin sa’ar tsundumawa cikin kogi mai mayunwatan kadoji, zarcewa cikin rijya mai masifaffiyar kasa ko fadawa kan kayar dake daji mai miyagun namun dawa.

Duk wannan tunanin na yi shi ne cikin ‘yan dakiku, rike da laima a dab da kofar jirgin, kafin na yi kundunbalar dirgowa daga jirgin don kubucewa daga mummunan hadarin da zai yi ba da jimawa ba.

Amma me? Addu’ar da na yi ta yi ta yi matukar tasiri, don kuwa lami-lafiya na sauka kan wani yashi dake cikin wani daji dake a gefen burtalin zuwa wani gari.

Kodayake dai na yi matukar farin ciki gami da godiya ga Allah dangane da saukata lafiya, amma ban tsawaita mamaki kan hakan ba. Abar da kawai ta tsawaita mamakina ita ce murya, wadda na ji a bayana, tana magana da harshen turanci, “Kamar a fim, amma na san gaske ne. Ka sauka lafiya?”

Na yi zumbur na juya yayin da mu ka yi tozali da mai maganar. Kyadildili ne mai gajeriyar faffadar fuska da mitsi-mitsin idanu. Ba na bukatar wasa kwakwalwata kafin na gane shi a matsayin mutum samfurin mutanen kasar Sin.

Na buda baki na amsa masa cikin harshen turancin, “Kwarai, kamar a mafarki. Na kuma gode. Zahiri na sauka lafiya.”

Ya gyada kansa, gyada kan da yanayinsa ya tuno mini da kadangare. Kana ya matso gare ni, ya miko mino hannu mu ka cafke, yayin da ya gabatar da kansa, “Sunana Wur Tsal.”

Na amsa masa, “Ni kuma nawa sunan shi ne Tukur Sarkin Yaki.”

“Sarkin Yaki?” Ya bida yana murmushi. “Ka ce ka zo garin da ya dace a lokacin da ya fi kowane dacewa.”

Na yamutse fuskata, “Ban ……..”

Ya katse ni ta hanyar daga mini hannu, “Jira mu karasa birnin Kussha. Za ka samu amsoshin duk tambayoyin da kake da su da kanka.” Kana zagaye ni, ya fara sassarfa ya nufi wani burtali. Sai da na dan yi jim, kafin na bi bayansa ni ma da sassarfar.

A lokacin da mu ka isa garin, mu ka kuma zagaya shi, sai mamakin dake zuciyata ya kara bunkasa, ganin cewa duk gidajen garin ba su da kofar shiga. Ban gane ma’anar hakan ba har sai, bayan da mu ka isa wani tafkeken dandalin da ya yi wa wani tafkeken gida kawanya. Tafkeken gidan ya zarta sauran gidajen garin ta fuskar tsayin katangar da ta zagaye gidan, ya kuma kamanci sauran gidajen garin ta fuskar rashin kofa. Akwai mutane maza da mata masu sifa irin ta Wur Tsal suna ta zarya a kofar gidan, shigen irin zaryar da ake yi a lokacin bikin sallah a kauye. Bambancin kawai shi ne, masu sayar da ababan makulashe a gurin duka abu guda suke sayarwa, wato kwanson kwakwa. Da na lura sai na ga masu sayen kwanson kwakwar a baki suke sakawa su kuma ci.

Wannan karon ban iya jurewa ba sai da na tambayi Wur Tsal, “Kwakuduba ce ta aure ku ne da baku da abinci sai kwanson kwakwa? Wannan ai sai ku raunana hakoranku.”

A nan Wur Tsal ya yi dariyar da ta nuna mini kwaftara-kwaftaran hakoransa, ya ce, “Dazu na ce maka ka zo garin da ya dace ne saboda sunanka sunan jarumai ne kuma garin nan ma garin jarumai ne. Mamallakin wannan tafkeken gidan da kake gani, mai suna Kussha, shi ne ya kafa garin nan. Kuma shi Kussha ya mutu ne a rana irin ta yau. Dalilin kenen da ya sanya duk rana irin ta yau ake irin wannan biki na baje kolin jarumta domin tunawa da irin jarumtar da ya nuna a rayuwarsa. Kuma tauna kwanson kwakwa a furzar da tukar na daya cikin bajimtoci biyu na wannan al’ada.”

Daganan sai ya je ya sayo kwanson kwakwar guda biyu. Tun ma kafin ya karaso gare ni ya balgaci kwanson ya fara taunawa, ji kake kurus. Da ya karaso sai ya miko mini daya daga cikin kwansunan, “Tauna don ……”

Na yi sauri na ce, “Azumi nake yi.”

A daidai wannan lokacin sai ga wasu mutane nan su biyar, kowane rike da kura, wadda aka sanya wa takunkumin baka. Dokacin kurayen sai muzurai suke yi kamar sa ci babu. Da na bukaci sanin abin da kurayen za su yi, sai Wur Tsal ya ce, “Kalaci.”

“Wane irin kalaci?”

Ya amsa, “Kalaci da wanda ba jarumi ba. Domin tun jiya rabon da a ba kurayen abinci. Nan ba da jimawa ba za a yaye masu takunkumin a kuma sake su. Muddin aka sake su kuwa, to mutanen gurin nan ba su da matsera sai gidan Kussha. Kowa can zai nufa, kuma, kai ma can ya kamata ka nufa.”

Cikin zakuwa na ce, “Ta yaya za a shiga gidan bayan ba shi da kofa?”

Wur Tsal ya ce, “Da kofa mana. Sai dai ba irin ta sauran garuruwa ba.”

“To a ina take, ya kai Wur Tsal?”

Ya ce, “Duk saman gidan ai kofa ce.”

Na daga kai na dubi doguwar katangar, kana na dawo da kaina gare shi, “To ai ban ga tsanin da za a tattaka don hawa katangar ba.”

Wur Tsal ya dube ni ya yi murmushi da zai ce, “Idan mutum shege ne shi a fagen jarumta to tashi kawai zai yi ya tsallake katangar ya dira cikin gidan. Kuma, shegantakar mutanen garin nan a kan jarumta take.”

A daidai lokacin da nake tunanin barin gurin tun da ni ba na tashi, sai aka yaye takunkumin kurayen nan, aka kuma sake su.”

Wane mutum! Ba sai mutanen gurin suka rinka tashi cikin gwaninta suna tsallake katangun gidan Kussha, suna shigewa cikin gidan ba! Cikin dan kankanen lokaci sai ya zama sai ni kadai na rage a gurin. Da dai na duba bayana da gefunana na kuma ga kurayen sun nufo ni baki bude, sai na yi kukan kura na nufi katangar. Da na kusa isa ga katangar, sai na rufe idanuwana, ina addu’a na daka uban tsalle. Amma ina! Addu’ata ba ta karbu ba, domin ko rubu’in katangar ban yi ba na ruguzo. Hakan kuwa ya kara wa kurayen kwarin gwiwar samun kalaci, don haka suka hanzarto. A lokacin da kurayen suka yi wo tashi za su dirar mini sai na kwalla ihun da ya zama mafarkin da ya farkar da ni daga barcin da nake yi.

Na yi zumbur na tashi zaune kan tattausar katifar, ina ta numfarfashi, yayin da garin ya yi tsit cikin talatainin dare. Daga nan sai na tashi na sauka daga kan gadon, na je na daura alwala, na yi nafila, kana na yi addu’o’i na kuma koma kan gadon da zummar kwanciya, amma ina! Maimakon haka sai tunanin mafarkin da na yi ya dawo mini, wanda hakan ya zama matursasin da ya tursasa ni alakanta manufar mafarkin da zahirin rayuwata.

Ni dai haifaffen birni ne gaba da baya, haka kuma ina cikin masu rufin asiri don daraktan mulki ne ni na wata karamar hukuma. Amma, da yake na fi sha’awar zama katoton bajimi a tsukakken garke fiye da zama madaidaicin bajimi cikin faffadan garken da manyan bajimai suka yi wa kaka-gida, sai na baro birnin na koma wata karamar hukuma da zama, inda bayan tsawon lokaci ina yi wa hakimin garin hidima sai bukatata ta biya, wato aka nada ni sarkin-yakin wannan karamar hukuma, domin babu taken da nake so a rinka zuga ni da shi kamar sarkin-yaki.

Anya kuwa wannan mafarkin ba manuni ne dake nuna mini cewa ina yin kwaina babu zakara ba? Kwai babu zakara mana, idan ba haka ba yaya za a yi na rinka amsa taken jarumin jarumai bayan buruntun bera ma firgita ni yake? In har ya zama wajibi in sarauci wani aiki mai ya sa wannan aiki ba zai dace da ni ba? Maimakon sarkin yaki, ya fi dacewa a kira ni da sarkin-yashe kudaden al’umma, tun da ni da ciyaman ne murguza-murguzan giwayen da ke kayar da baragen kason waccan karamar hukuma, a duk watan duniya. Anya kirana da sarkin-yaki bai zamo tamkar lullubar kura da fatar akuya ko yin ungulu da kan zabuwa don tabbatar tsarin nan na kashin dankali ba?

Amsa ta ga hakan ita ce, idan hakan gaskiya ne to ba ni kadai ya shafa ba. Domin kuwa, yawancin ‘yan siyasa kan yi karya da sunan talaka don kururuta mulkinsu, wasu cikin masu rawani da wasu cikin cikin masana addini kan yi amfani da sunan Allah da dadadan kalamai don martaba kansu, mawaka kan kambama manya don zakaka miyarsu, marubuta kan sanya batsa cikin rubutu don dabbaka kasuwar littafansu, da yawa cikin masu duba jarrabawa kan duba ta yadda suka so don bayar da dama ga ‘ya’yan masu kudi don su fi tabbata a mulkin al’umma ta hanyar tabbata a karatun jami’a ba. Anya ma ban taba jin wani mamallakin makarantar kudi yana cewa taimaka wa gwamnati suke yi wajen samar da nagartaccen ilmi ba, bayan shi kansa da dukkanin manyan kasar nan makarantun gwamnatin suka yi suka kuma zama abin da suka zama a yau ba? Hakika na ji shi. Abin da kawai bai ce ba shi ne samuwar makarantun nasu ne ke kara kassara makarantun gwamnatin da ‘ya’yan talakawa ke halarta ba. Anya ban taba sauraron wani masanin halayyar ‘yan Adam, wanda ya lissafo matsalolin zaluncin masu mulki kuma mirsisi ya ki cewa tsadanta karatu gami da toshe damar shigar ga wasu da kuma mugun nufi da yawancin mallaman , ciki har da shi, ke yi na sababin karuwar laifuffuka a kasar nan ba? Hakika na ji. Anya ma ban taba ganin wani talaka yana allawadai da irin zaluncin da shugabanni kan yi bayan shi ma yana zaluntar sauran talakawa ta hanyar zubar da shara a wajen gidansa ba tare da ya kone ta ba? Hakika na gani! Na ma ga talakan da yake sakin tumakansa kullum su fito, bayan ya san dabbobi na iya shiga gidan makwabcinsa su yi masa barna ba.

A nan sai zuciyata ta washe. A kalla dai ina da ‘yan uwa barjak, wadanda na fi wasu, wasu kuma suka fi ni kan waccan halayya ta takidin gina kai ko da kuwa za a danne na kasa.

Gamsuwa da cewa waccan mafarki nawa kamar fadakarwa ne gare ni ya sanya na tambayi kaina, shin ko na fadaku da fadakarwar wannan mafarki kuwa? Sanin da na yi na cewa naira naira ce ya sanya ni barin tambayar babu amsa. Har sai lokacin da kason karamar hukumar da nake wa darakta ya zo. Idan na iya jajircewa da cewa ban yarda a hada baki da ni a sace kudaden al’umma ba, na kuma iya dagewa da a sarrafa wannan kudi ta hanyoyi mafiya dacewa, to dole in girmama kaina. Idan kuwa na iya yin wani abu sabanin haka to mutuncina zai cigaba da zubewa a idanuwana saboda na taka rawa wajen nisanta maji kishirwa daga rafi zuwa kololuwar hamada.